Ƙungiyar Taliban ta sanar da hana mata zuwa jami’a a Afghanistan



Afghan Female Students

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

A watannin baya ne mata da sauran ɗalibai a Jami’ar Kabul suka sake komawa karatu bayan Taliban ta ƙwace iko

Ƙungiyar Taliban ta sanar da hana mata zuwa jami’o’i a ƙasar Afghanistan, a cewar wata wasiƙa daga ministan ilmi mai zurfi.

Ministan ya ce wannan mataki zai ci gaba har zuwa lokacin da za a ji sanarwa ta gaba. Ana sa ran wannan mataki zai fara aiki ne nan take.

Sanarwar ta kuma taƙaita wa mata hanyoyin samun ƙa’idajjen ilmi, don kuwa tun tuni Taliban ta ware mata daga halartar mafi yawan makarantun Sakandire.

Wata ɗalibar Jami’ar Kabul ta faɗa wa BBC cewa tun bayan jin wannan labari take ta sharɓar kuka.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like