Ƴan matan Dapchi: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin Rundunar Soja Da Gwamnatin Yobe Kan Ƴan Matan Dapchi


Rundunar Sojan Nijeriya ta musanta zargin gwamnatin Yobe kan cewa sakacinsu ne ya janyo mayakan Boko Haram suka samu nasarar arcewa da ‘yan Matan Sakandaren Dapchi na jihar a ranar Litinin.

Kakakin Rundunar, Birgediya Janar Jude Chukwu ya ce an girke sojoji a wani wuri mai nisan kilomita 30 daga makarantar kafin harin. Tuni dai, wasu suka yi Allah wadai kan wannan cacar bakin a daidai lokacin da ya dace bangarorin biyu suka hada kai don ganin an ceto ‘yan Matan.

You may also like