Gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje ya kai garzaya fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da shaida masa babbar barazanar da ya ke fuskanta sakamakon yunkurin mamaye jihar da Boko Haram ke shirin yi.
“Na kawowa shugaban kasa ziyara ne akan halin tsaron jihar Kano, karya kashin bayan su da aka yi a can inda suke shine suke kwararowa nan daga Sambisa domin kafa sansanin su a nan don ci gaba da gudanar da ayyukan su”.