Abin da ya sa wasu mazan Indiya suka yi tattaki don neman aure



ALPHONSE VIMALRAJ

Asalin hoton, ALPHONSE VIMALRAJ

Bayanan hoto,

Mallesha DP ya ce mata kusan 30 ne suka ki shi a cikin shekaru da suka gabata

A watan da ya gabata, wasu maza a jihar Karnataka da ke kudancin Indiya sun yi tattaki mai nisan kilomita 120 don ziyartar wani gidan ibada domin su yi addu’ar samun matan aure.

Yunkurin nasu ya haifar da mamaki a yanar gizo, amma masu fafutuka sun ce hakan na nuni da zurfafa batutuwan zamantakewa da tattalin arziki a yankin.

Yawancin mazajen da suka shiga wannan tattakin – an fara shi ne da mahalarta 30, inda kuma ya ƙare da guda 60 – sun kasance manoma daga gundumar Mandya ta Karnataka.

Yawan jima’i a lokacin haihuwa a yankin ya kasance na tsawon gwamman shekaru – masu fafutuka sun ce wannan shi ne dalili da ya sa maza da yawa ke wahala wajen yin aure.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like