‘Abin kunya ne Buhari ya mika wa jam’iyyar da ba APC ne ba mulki a 2023’



Abdullahi Adamu APC chair
Bayanan hoto,

Abdullahi Adamu Shugaban jam’iyyar APC ta Najeriya

A Najeriya, jam’iyyar APC mai mulkin kasar ta yi fatali da sukar da wasu ke yi cewa shugaba Muhammadu Buhari na janye jiki daga tafiye-tafiyen da ake yi na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam`iyyar APC mai mulki, Bola Ahmed Tinubu.



Jam’iyyar ta ce a matsayinsa na shugaban kasa bai dace ya jingine aikin sa na jagorancin al’ummar Najeriya saboda yakin neman zabe ba.



Senata Abdullahi Adamu shi ne shugaban jam’iyyar APC na Najeriya, kuma a tattaunawar da ya yi da BBC, ya ce sun gamsu da yakin neman zaben, kuma ba sa shakkar abokan hamayyarsu:



“Abubuwa na tafiya yadda muke so, domin idan ba za mu sa rashin godiya ga Allah ba ne, dukkan wanda ke bin tafiyarmu, alamomi da ke zahiran ba badilan wadanda Allah ke nuna mana, mun aganin nasara.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like