Abu hudu da ya sa ba zamu saurare koken ɗage lokacin daina karban tsoffin kuɗin naira ba



MUHAMMADU BUHARI

Asalin hoton, Presidency

Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta Najeriya ta fayyace wasu dalilai hudu da suka sa ba za ta saurari batun kara wa’adin daina karbam tsoffin kudin naira ba a kasar, tana mai cewa ba wai saboda talaka ya shiga cikin matsi ba ne.

Gwamnatin ta ce tabbas shugaba Buhari yana sauraron koke-koken al’umma kan wannan sauyi da matsin da suka shiga, kuma ana duba hanyoyin da ya kamata a bi domin saukaka wahalhalun talaka da kyautata musu.

Sai dai sauyin a wannan lokaci ya zama wajibi a cewar kakakin shugaban Mallam Garba Shehu.

Garba Shehu ya ce abu na farko da ya kamata a sani shi ne ba wai an bijiro da wannan tsari ba ne saboda a galazawa mutane ko hanasu kasuwanci ko cigabansu ba ne, amma akwai bukatar a fahimci anyi hakan ne saboda masu sace dukiyar kasa da aikata rashawa.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like