Adadin mutanen da basu da aiki ya karu  a cewar hukumar kididdiga ta ƙasa


Yawan mutanen da basu da aikin yi ya karu daga kaso 16 cikin ɗari  a zango  na biyu na wannan shekara zuwa kaso 18.8 cikin ɗari a zango na uku na wannan shekara.

Hakan na kunshe ne cikin rahoton aikin yi da hukumar kididdiga ta kasa NBS  ta fitar a ranar juma’a.

Adadin marasa aiki ya karu daga mutane miliyan  13.5 a zango na farko na wannan shekara zuwa miliyan 17.7 a zango na biyu inda ya kuma karu zuwa miliyan 18. a zango na uku na wannan shekarar.

Hakan dai na zuwa ne duk da ƙoƙarin da gwamnati take na samar da guraben aiyukan a bangaren kamfanoni masu zaman kansu.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like