Adamawa: Zaɓen da aka kammala ƙura ba ta kwanta ba



Adamawa election

Kwana ɗaya bayan damƙa shaidar cin zaɓe ga Ahmadu Umaru Fintiri, ɗan takarar da ya yi nasara a zaɓen gwamnan jihar Adamawa kan wa’adi na biyu, har yanzu dambarwa da kuma zarge-zarge, ba su ƙare ba.

Batu na baya-bayan nan, shi ne wata sanarwa da hukumar zaɓe ta INEC ta fitar tana musanta wasu zarge-zarge da ake alaƙantawa da jami’an da ta aika su gudanar da zaɓe a jihar.

Ta ce zargin da wani ko wata ‘yar takara ke yi cewa – jami’an zaɓen Adamawa cikin dare sun kai wata ziyara gidan gwamnatin jihar – ba gaskiya ba ne.

Haka zalika, sanarwar wadda kwamishinan INEC kan harkokin yaɗa labarai da wayar da kan masu zaɓe, Festus Okoye ya fitar, ta ce shi ma batun cewa an ba wani ɗan takara jerin sunayen jami’an sanar da sakamakon zaɓe na jihar, ba gaskiya ba ne.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like