Al Nassr na sa ran Ronaldo zai gama shiga kulob ɗin a yuro 200m



Ronaldo

Asalin hoton, Getty Images

Kulob ɗin Saudiyya Al Nassr na sa rai ɗan wasan gaba na Portugal Cristiano Ronaldo, mai shekara 37 zai kammala sa hannu don koma wa ƙungiyar nan da ƙarshen shekara. Tsohon ɗan wasan Manchester United ɗin zai sa hannu ne kan wata yarjejeniya ta tsawon shekara biyu a yuro miliyan 200. 

Ɗan wasan gaban Brazil mai buga wa ƙungiyar Arsenal Gabriel Martinelli, mai shekara 21, na shirin sa hannu kan wani sabon kwanturagi da kulob ɗin nasa a kan fam 200,000-duk-mako. 

Zakarun Faransa Paris St-Germain na sa rai, nan da ‘yan kwanaki za su sake tabbatar da zaman ɗan wasan gaban Argentina mai shekara 35 Lionel Messi a kulob ɗin. Kwanturagin gwarzon da ya lashe Gasar Kofin Duniya za ta ci gaba har lokacin zafi amma yana da damar ci gaba da tattaunawa da wasu ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa a wajen Faransa daga ranar 1 ga watan Janairu. 

Ƙungiyar Arsenal da Atletico Madrid kowaccensu na da burin ɗaukar ɗan wasan tsakiyar da suka ci wa Argentina Gasar Kofin Duniya mai taka leda a Brighton Alexis Mac Allister, ɗan shekara 23



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like