Alamomin cutar Marburg wadda ta ɓulla a Afirka



Cutar Marburg

Asalin hoton, Getty Images

A ranar Litinin 13 ga watan Janairu ne ƙasar Equatorial Guinea ta tabbatar da ɓullar cutar Marburg karon farko a ƙasar.

Cutar ta fara ɓulla ne a lardin Kie Ntem da ke yammacin ƙasar.

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutum tara, tare da samun mutum 16 da ke ɗauke da cutar a Equotorial Guinea, da kuma samun rahotonnin alamomin da ke nuna cewa mutum na ɗauke da cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta aike da samfurin jini zuwa cibiyarta da ke ƙasar Senegal domin gwajin tabbatarwa.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like