Alawus din da aka biya tawagar Senegal ya haifar da cece-kuce



.

Asalin hoton, OTHER

Matakin Shugaban Senegal na biyan tawagar kwallon kafar kasar alawus masu kauri ya haifar da cece-kuce.

Shugaba Macky Sall ya ce za su biya tawagar kudaden da suka yi alkawarin basu idan suka kai zagayen quarter-finals, duk da basu iya tsallake zagayen 16 ba.

Dama gwamnati ta yi wa Teranga Lions alkawarin kudade masu yawa idan suka kai zagayen quarter-finals, to amma sai gashi Ingila ta doke su 3-0 a zagayen kungiyoyi 16.

” Za mu biya duka kudaden da muka yi alkawarin bai wa tawagar,” in ji Shugaba Sall.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like