Amurka ta ce a tsagaita wuta a Sudan bayan kashe kusan mutum 200



US top diplomat

Asalin hoton, Getty Images

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya tattauna da babban hafsan sojin Sudan, Abdel Fattah al-Burhan da jagoran dakarun kai ɗaukin gaggawa, Mohammed Hamdan Dagalo yayin da ake ci gaba da kafsa faɗa tsakanin dakarun shugabannin biyu na Sudan.

Kimanin 185 ne aka kashe tun bayan ɓarkewar faɗan ranar Asabar.

Anthony Blinken ya wallafa wani saƙon Tuwita da ke cewa yana jaddada buƙatar gaggawa ga dakarun shugabannin biyu su tsagaita.

Ya nanata cewa muhimmancin haka shi ne a tabbatar da tsare lafiyar jami’an diflomasiyya da kuma ma’aikatan ba da agaji.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like