Hukumar da ke sa ido a a kan kamfanonin sadarwa ta Najeriya, NCC ta dakatar da shirinta na kara kudin data ga masu amfani da wayar salula.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Tony Ojobo ya aikewa manema labarai, ya ce sun dauki matakin ne sakamakon sukar da suke sha daga wurin jama’a.
A cewarsa, hukumar ta umarci kamfanonin sadarwa su dakatar da kara kudin datar kan masu amfani da su.