An daure ‘yan majalisa biyu bayan sun daki wata ‘yar majalisa mai juna biyu



Senegal's parliament brawls after woman MP hit by colleague

Asalin hoton, Getty Images

Wasu ‘yan majalisar kasar Senegal biyu za su shafe watanni shida a kurkuku bayan ta same su da laifin hambarar wata ‘yar majalisa mai juna biyu a ciki yayin da ake tafka muhawara a zauren majalisar kan kasafin kudin kasar.

‘Yan majalisar – wadanda dukansu maza ne – sun kai wa Amy Ndiaye hari ne bayan da ta soki wani shugaban addini kuma jagoran wata jam’iyyar siyasa na kasar.

Alkalin kotun da ta yanke wannan hukuncin ya kuma ci ‘yan majalisar biyu – Mamadou Niang and Massata Samb – su biya Uwargida Ndiaye CFA miliyan biyar (dala 8,100.00) domin cin mutuncinta da suka yi.

Harin da suka kai wa ‘yar majalisar ya janyo kakkausar suka a fadin kasar, kuma ya haifar da wata mahawara kan ‘yancin mata.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like