Shugaban Rundunar ‘Yan sanda na kasa, Ibrahim Idris ya bayar da umarnin janye dukkan ‘yan sandan da ke gadin manyan jami’an gwamnati wanda ya hada har da ‘yan siyasa.
Da yake karin haske kan matakin, Shugaban ‘yan sandan ya ce umarnin ya shafi ‘yan kasuwa da manyan kamfanonin wadanda ‘yan sanda ke yi masu gadi.