An kai wa ofisoshinmu hari sau 50 cikin shekara uku – Inec



Ofishin jakadancin China

Asalin hoton, Inec

Bayanan hoto,

Hedikwatar Inec a Jihar Imo da aka ƙona a watan Disamba

Hukumar zaɓe a Najeriya ta ce an kai wa ofisoshinta hari a faɗin ƙasar sau 50 daga 2019 zuwa 2022.

A cewar bayanan da National Electoral Commission (Inec) ta fitar ranar Juma’a, hare-haren sun afku a jiha 15 jimilla, waɗanda suka haɗa da Imo (11), Osun (7), da Enugu (5), da Akwa Ibom (5), da Ebonyi (4), da Cross River (4), da kuma Abia (4).

Sauran su ne: Anambra (2), Taraba (2), Kaduna (1), Borno (1), Bayelsa (1), Ondo (1), Lagos (1), Ogun (1).

Shekarar 2020 ce shekarar da aka fi samun hare-haren inda aka kai sau 22, sai 2021 mai 12, da kuma 2019 da 2022 da aka kai hari sau takwas-takwas.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like