Kawancen jam’iyun siyasa na FRDDR a Nijar, sun yi kira ga shugaban kasar, Mahamadou Issoufou da ya yi murabus daga mukaminsa.
‘Yan adawar dai na zargin shugaban ne da kasawa da rashin iya mulki. Sun kuma ce tunda shugaban ya hau mulki a 2016, kasar ta fada cikin halin kaka ni ka yi.