An samu ɓullar zazzaɓin Lassa a jihar Ondo.


Gwamna Oluwarotimi Akeredelu na jihar Ondo ya tabbatar da ɓarkewar cutar Lassa a Jihar, yace gwajin da akayi a dakin  gwaje-gwajen kimiya ya tabbatar da mutane 36 dake ɗauke da cutar da suka haɗa da 9 waɗanda suka mutu.

Akeredelu wanda ya bayyana haka a Akure cikin wani jawabi na kai tsaye da aka watsa ta kafafen yaɗa labarai  dake jihar a daren ranar Asabar, yace mutane 108 ake zargin sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa a ƙananan hukumomi 8 dake jihar.

“79 daga cikin wadanda ake zargin sunkamu da cutar bayan gwajin da akayi, hadi da mutane 9 da suka mutu.

“Marasa lafiyar ana kula da su a cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Owo  ya yin da ake gwajin tabbacin kamuwa da cutar a asibitin kwararru na Irua dake jihar Edo.

Gwamnan ya ƙara da cewa yanzu haka gwamnati ta fara bikin gangamin wayar da kan jama’a  kan yadda za a kaucewa kamuwa da cutar.

You may also like