An yanke wa ɗan majalisa hukuncin ɗauri saboda ‘ɓata suna’



...

Asalin hoton, Getty Images

Kotu a Indiya ta yanke wa jagoran ƴan adawa na ƙasar Rahul Gandhi hukuncin ɗauri na shekara biyu bayan samun sa da laifin zubar da mutunci.

Wata kotu a jihar Gujarat ce ta kama Gandhi da laifi kan kalaman da ya yi a shekarar 2019 a kan firaminista Narendra Modi, lokacin wani gangami na siyasa.

A yanzu ɗan adawar na da tsawon kwana 30 domin ya ɗaukaka ƙara.

Ɗan adawar wanda ɗan majalisa ne a halin yanzu ya halarci zaman kotun a lokacin da aka yanke hukunci.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like