An yi kuskure wajan raba mukamai a majalisar dattawa -in ji Ndume



 Ndume

Asalin hoton, senate

Bayanan hoto,

Sanata Ali Ndume

Wata baraka ta kunno kai a majalisar dattawan Nijeriya inda rahotanni ke cewa an samu wasu sanatoci da ke shirin tsige shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio.

Rahotannin sun ce sanatocin sun nuna rashin jin dadi a kan abinda suka kira kusancin ‘shugaban majalisar da fadar shugaban kasa’.

Sai dai sanata Mohamed Ali Ndume wanda shi ne mai tsawatarwa a majalisar dattawan Nijeriyar ya shaida wa BBC cewa rikicin na da nasaba da korafin da wasu sanatocin su ka yi a kan cewa an nuna mu su wariya wajan rabon mukaman shugabancin kwamitoci da majalisar ta yi a baya baya nan.

Ya kuma amince da cewa an yi kuskure a rabon mukaman amma barakar da aka samu ba sabuwar aba ba ce a cewarsa:



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like