Ana ce-ce-ku-ce kan gina masallaci mafi tsada a Masar



Sabon Masallacin

Asalin hoton, ALAMY/REUTERS

Bayanan hoto,

Sabon Babban Massallacin na Masar zai iya daukar masallata dubu 107

Masar ta bude wani katafaren masallaci wanda ya kafa tarihi ta fannoni da dama da kuma kasancewa na biyu mafi girma yanzu a Afirka, a sabon babban birnin kasar, sai dai kuma jama’a na ta suka a kan yawan kudin da aka kashe.

Gwamnatin kasar tana gina sabon birnin na mulki ne a cikin hamada, a wani wuri da ke da nisan kilomita 45, gabas da Alkahira, domin rage yawan mutane daga babban birnin na yanzu wanda ya cika ya batse da jama’a.

Sai dai kuma bude sabon masallacin tare da wata babbar cibiyar harkokin Musulunci ta janyo ce-ce-ku-ce da suka daga mutane da dama a shafukan sada zumunta da muhawara.

Jama’a na kokawa da ayyukan kan dimbin kudin da aka kashe yayin da kasar ke fama da hauhawar farashin kayayyaki da ayyuka, inda lamarin ya wuce kashi 30 cikin dari a watan Maris din nan.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like