Ana fargaba kan shirin Saudiyya na zartar da hukuncin kisa kan wasu ‘yan Nijar



Bazoum

Asalin hoton, OTHERS

Bayanan hoto,

Gwamnatin Nijar ba ta ce komai ba kan ceto mutanen da Saudiyya za ta kashe

A  jamhuriyar Nijar masu fafutukar kare hakkin dan’Adam sun bukaci gwamnatin kasar ta saka baki don dakatar da zartar da hukuncin kisa da kasar Saudiyya ke shirin yi kan wasu ‘yan Nijar hudu da ta kama da zargin fataucin miyagun kwayoyi.

Masu fafutukar na kokawa  ne da yadda gwamnatin ta Nijar ta yi gum da bakinta suka ce akwai bukatar gwamnatin ta saka baki  wajen ceto rayuwar mutanen.

Rahotanni sun bayyana cewa hukumomin Saudiyya sun damke maza biyu da mata biyu ne ‘yan Nijar a filin jirgin sama na Jeddah da ke kasar ta Saudiyya.

Ana zargin mutanen ne da fataucin miyagun kwayoyi da Saudiyyar ta haramta.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like