Ana samun ƙarancin haihuwa tsakanin ma’aurata – WHO



Mace mai ciki

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta yi kiran a dauki matakin gaggawa kan magance ƙaruwar matsalar rashin haihuwa.

A wani sabon rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta fitar, ta ce sama da ɗaya bisa shida na baligai ne ke gaza samun haihuwa a wani mataki na rayuwarsu.

Daraktar fannin bincke kan lafiyar ma’aurata da haihuwa a hukumar, Pascale Allotey ta ce akwai ƙarancin kula da fannin rashin haihuwa.

WHO ta ce akwai buƙatar a gaggauta bijiro da hanyoyin samar da waraka ga matsalar rashin haihuwa tsakanin ma’aurata.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like