Ana tuhumar mabiya coci da laifin karan-tsaye ga kundin tsarin mulki



...

Asalin hoton, AFP

An kama ɗaruruwan mabiya cocin Orthodox a Habasha a ‘yan kwanakin nan bayan taƙaddamar da suke ta yi da hukumomi, kamar yadda lauyoyi da ke wakiltar cocin suka faɗa wa BBC.

Shugaban lauyoyi da ke wakiltar cocin na Orthodox, Ayalew Bitanie, ya ce zuwa yanzu an tsare mutane kusan 200.

Ya ce yawancin waɗanda aka tsaren, an ajiye su ne a Addis Ababa, babban birnin ƙasar, da wasu larduna da ke kusa da birnin, sai dai, an tafi da wasu zuwa wani sansanin soji da ke da nisan kilomita 200 da gabashin Addis Ababa.

Sai dai, BBC ba ta tabbatar da gaskiyar wannan iƙirarin ba.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like