APC na amfani da kotunan Najeriya don yi wa dimokraɗiyya karan-tsaye – PDP



Atiku Abubakar

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Atiku Abubakar (na biyu daga dama) ne ya yi wa PDP takarar shugaban ƙasa a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, wanda kotu ta bai wa Bola Tinubu na APC nasara

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya, ta bayyana hukunce-hukuncen da kotunan ɗaukaka ƙara suka yi, inda suka ƙwace nasarar wasu gwamnoni a matsayin “karan-tsaye” ga dimokraɗiyya.

Jam’iyyar adawar na zargin APC mai mulkin Najeriya ne da “amfani da ƙarfin iko” wajen tanƙwara hukuncin kotunan, zargin da APC ta musanta.

“Shari’ar Najeriya ta zama kamar rawar ‘yan mata yanzu; idan an yi gaba, sai a koma baya,” in ji Mataimakin Sakataren PDP na Ƙasa, Ibrahim Abdullahi.

A makon jiya ne, kotunan ɗaukaka ƙara suka yanke hukuncin soke nasarar gwamnoni uku na jihohin Filato, da Zamfara, da Kano – dukkansu a arewacin ƙasar. PDP ce ke mulki a jihohin Zamfara da Filato, yayin da NNPP ke mulkin Kano.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like