Arsenal ta samu damar bai wa Man City tazarar maki takwas



Mikel Arteta

Asalin hoton, Getty Images

Arsenal za ta karbi bakuncin Crystal Palace a wasan mako na 28 a gasar Premier League a Emirates ranar Lahadi.

Palace za ta buga wasan karkashin kociyan matasanta ‘yan shekara 21, Paddy McCarthy, bayan da ta kori Patrick Vieira.

Albert Sambi Lokonga ba zai fuskanci kungiyarsa ba, yayin da ake auna koshin lafiyar Will Hughes da James McArthur, da kyar idan gola, Vicente Guaita zai yi karawar.

Mai tsaron bayan Arsenal, Takehiro Tomiyasu da kuma William Saliba an sauya su, wadanda suka ji rauni a karawa da Sporting a Europa League.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like