Ba a rana daya zan magance matsalar Chelsea ba – Lampard



Frank Lampard

Asalin hoton, Getty Images

Frank Lampard ya ce baya jin za a magance matsalar Chelsea a rana daya, bayan da ya fara da kafar dama a Wolverhampton.

Lampard wanda ya ja ragamar Chelsea a karon farko a matakin rikon kwarya, ya yi rashin nasara 1-0 a gidan Wolves a wasan mako na 30 a Premier ranar Asabar.

Wasan farko da ya shugabancin Chelsea tun bayan wata 27 da aka kore shi a Stamford Bridge, Thomas Tuchel ya maye gurbinsa.

Chelsea ta kasa zura kwallo a raga a wasa uku a jere kenan, karo na 11 da aka doke ta a babbar gasar tamaula ta Ingila ta kakar nan.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like