Ba mu yarda da sakamakon zaɓen gwamnan Kano ba – APC



Gawuna

Asalin hoton, FACEBOOK/NASIRU GAWUNA

Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC mako daya ta sake nazari kan sakamakon zaben gwamna na jihar da aka yi ranar 18 ga watan Maris.

APC ta bayyana haka ne a taron manema labaran da ta yi yau Talata inda ta bakin lauyanta na jiha, Barista Abdul Fagge ta ce baturen zaben ya yi kuskuren fahimtar dokar zabe wajen banbance sokewa sakamakon wasu wurare da aka yi sanadin tashin hankali da kuma zabe fiye da kima.

APC dai ta ce sam ba ta yadda da hanyar da aka bi wajen sanar da sakamakon zaben ba har aka bayyana Abba Kabir a matsayin zababben gwamna a don haka ta nemi a gaggauta sake yin zagaye na biyu na zaben.

Sai dai a cewar lauyan, baturen zaben ya yi la’akari ne kawai da batun tashin hankali wajen kare tazarar da ke tsakanin yan takara biyu – Abba Kabir Yusuf na NNPP da Nasir Gawuna na APC.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like