Ba wani siddabaru nake yi ba a Man City in ji Guardiola



Pep Guradiola

Asalin hoton, Getty Images

Pep Guardiola ya ce ba wani siddabaru yake yi ba a Manchester City da har ya lashe Champions League a karon farko.

City ta dauki Premier League da FA Cup a bara, wadda ta zama ta uku a Ingila da ta lashe kofi uku, wadda ta ci Inter Milan 1-0 a Champions League a wasan karshe.

City za ta fara kare kofin da ta dauka a bara da yin wasan farko a cikin rukuni ranar Talata, inda za ta karbi bakuncin Red Star Belgrade a Champions League.

”Abu ne mai sauki. Da zarar ka dauki kofin farko hanya ta buɗe” in ji Guardiola.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like