Ba zan yi wa sabon Gwamnan Kano katsalandan ba — Kwankwaso



Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a Najeriya, Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ba zai yi wa Gwamnan Kano mai jiran gado, Abba Kabir Yusuf, katsalandan ba a harkar tafi da mulki.

A wata hira da BBC, Kwankwaso, wanda shi ne jagoran jam’iyyar ta NNPP na kasa, ya ce idan gwamnan mai jiran gado ya nemi shawararsa zai ba shi.

Sai dai ya ce a matsayinsa na dan Kano zai rinka ankarar da gwamnatin a duk lokacin da ya ga an kauce hanya.

Jagoran jam’iyyar ta NNPP, ya ce “ Ai shi mulki ko mai shararka ne ka ba shi to ka koma waje daya in ya nemi shawararka ka bayar, idan kuwa bai nema ba sai ka yi shiru.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like