BH Sun kashe mutane 7 a wani harin kunar bakin wake kan wani masallaci a Yobe


Wasu motoci da sojoji suka samu a sansanin BH dake Sambisa

Wata mace yar kunar bakin wake da ake zaton yar kungiyar Boko Haram ce ta tarwatsa kanta a bakin wani masallaci dake yankin Fulatari a Buni Yadi dake karamar hukumar Gujba ta jihar Yobe a ranar Juma’a inda suka kashe mutane 7.

Harin na Yobe na zuwa ne Kasa da mako biyu bayan da aka sace wasu yan mata 110 a makarantar sakandaren Yan Mata Ta  Kimiyya Da Fasaha dake Dapchi.

Wata majiya a rundunar soji ta shedawa jaridar The Cable cewa harin ya faru ne da misalin karfe 5:30  lokacin da aka taru domin yin sallar asuba.

A cewar majiyar an dauke wadanda suka jikkata ya zuwa asibiti.

“Fashewar bom din gaskiya ne, sun rasa mutane 7 a harin, 28 kuma suka jikkata.ya faru da safiyar nan lokacin sallar asuba da misalin Æ™arfe 5:30. Akwai wadanda suka jikkata da dama har yanzu   suna daukar su zuwa asibiti. Iya kacin abinda zan iya cewa kenan a yanzu,” a cewar majiyar.

You may also like