Bola Tinubu: Zan cire tallafin man fetur ko za a yi zanga-zanga a Najeriya



Tinubu

Asalin hoton, Twittter/@officialABAT

Dan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu, ya sha alwashin janye tallafin man fetur da zarar ya zama shugaban kasar.

Tinubu ya bayyana haka ne ranar Alhamis da daddare a yayin da yake gudanar da taro da wasu ‘yan kasuwar kasar.

“Dokar man fetur tana nan kuma za mu duba ta a karo na biyu domin sauke nauyin da ke kanmu kuma duk zanga-zangar da za a yi, za mu cire tallafin man fetur,” in ji Tinubu.


Ya kara da cewa: “Za mu dauki matakai masu tsauri, wannan shi ne batun gaskiya. Don haka wajibi ne mu cire tallafin man fetur.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like