Buhari  ya karbi bakuncin yan matan sakandaren Dapchi 


Shugaban kasa Muhammad Buhari a ranar Juma’a ya karbi bakuncin  yan matan sakandaren Dapchi da aka sako a ranar Laraba.

An dauki yan matan a jiya Alhamis zuwa Abuja daga  Maiduguri cikin wani jirgin saman soji.

A ranar Laraba ne ya’yan kungiyar ta Boko Haram suka dawo da yan matan garin Dapchi inda suka dauke su tun da farko.

Ministan yaɗa labarai Alhaji Lai Muhammad ya musalta jita-jitar da mutane wasu  suke yadawa cewa gwamnati ta biya diyya kafin a sako yan matan.

You may also like