A wani mataki na wanzar da zaman lafiya, Shugaba Muhammad Buhari ya nada wani kwamiti kan tallafawa duk wadanda suka yi asara a sakamakon rikicin Fulani makiyaya da manoma a duk fadin kasar nan.
Da yake karin haske kan aikin kwamitin, Mataimakin Shugaban Kaaa, Yemi Osibanjo wanda kuma shi ne Shugaban kwamitin ya ce, kwamitin zai duba yadda za a samar da ababen more rayuwa a yankunan da suka yi fama da rikice rikicen makiyayan