Buhari ya sauka a birnin Paris 


Shugaban kasa Muhammad Buhari tare dq yan tawagarsa  sun isa birnin Paris na ƙasar Faransa domin halartar wani taro na  kasashe 50 kan sauyin  yanayi.

Shugaban wanda ya samu rakiyar gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, gwamnan jihar  Ondo, Rotimi Akeredelu da kuma na jihar Adamawa Jibrila Bindow.

Shugaban ya tashi daga birnin Kano bayan da yayi hutun karshen mako a mahaifarsa ta Daura.

You may also like