Buhari ya yi ganawar sirri da Tinubu a birnin Landan


Shugaban kasa,Muhammad Buhari a ranar Talata ya yi wata ganawar sirri da jagoran jam’iyar APC na kasa, Bola Ahmad Tinubu, a birnin Landan.

Mai bai wa shugaban kasar shawara kan kafafen sadarwar zamani,Bashir Ahmad shi ne ya bayyana haka a shafinsa na Twitter @BashirAhmad.

Mai taimakawa shugaban kasar ya rubuta: ” shugaban kasa Muhammad Buhari ya karbi bakuncin jagoran jam’iyyar APC na kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu yau a birnin Landan.”

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito cewa Buhari wanda ke ziyarar aiki a birnin Landan, a ranar Laraba ne ya gana da Akbishop na Canterbury, Justin Welby inda ya bayyana masa dalilinsa na son sake tsayawa takarar shugaban kasa.

You may also like