Shugaba Muhammad Buhari ya jajantawa iyalan tsohon Gwamnan Kaduna, Lawal Kaita wanda Allah ya yi masa rasuwa a jiya Talata bayan ya yi fama da rashin lafiya.
Kakakin Shugaban Kasa, Garba Shehu ya bayyana cewa Buhari ya bayyana marigayin a matsayin dattijo Ina ya nemi iyalansa da su yi hakuri da wannan rashi tare da yi masa fatan samun rahamar Ubangiji.