Ce-ce-ku-ce ya barke tsakanin PENGASSAN da IPMAN kan tsadar fetur



.

Wata taƙaddama ta barke tsakanin kungiyar manyan ma’aikatan mai ta PENGASSAN da kungiyar manyan dillalan man fetur a Najeriya kan tsadar da mai ke yi a ƙasar.

Kungiyar manyan ma’aikatan mai a Najeriya ta PENGASSAN ce dai ta buƙaci hukumomin tsaron  kasar da su dakatar da dillalan man fetur a ƙasar daga boye mai don sayar da shi sama da farashin gwamnati.

Shugaban kungiyar na kasa Comrade Festus Osifo ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a Abuja.

Ya ce: “ƙarancin man fetur din da ake fama da shi a kasar da ya-ƙi-ci, ya-ƙi cinyewa, ya zama abin damuwa ga ‘yan Najeirya saboda yadda ya fi shafar su, inda suke sayen man fetur din fiye da ainihin farashin da gwamnatin ƙasar ke sayarwa.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like