Da Najeriya ta je Qatar 2022 da an yi mata cin wulakanci- Siasia



Siasia

Asalin hoton, OTHER

Tsohon kocin Super Eagles Samson Siasia ya ce ko da Najeriya ta je Qatar ba bu abunda za ta tabuka.

Siasia ya musanta ikirarin da wasu ke yi cewa irin rawar da wasu kasashe a nahiyar Afrika suka taka a gasar Najeriya ma za ta iya takata, da ace ta samu zuwa gasar ta kofin duniya.

To amma tsohon dan wasan tsakiyar, wanda ya lashe kofin nahiyar Afrika a 1994, ya ce tawagar da ta kasa cire Ghana a wasan share fage, babu abunda zata iya tabukawa a Qatar, gara ma ba ta je ba.

Kasashen Kamaru da Tunisia sun taka rawar gani duk da basu samu tsallakewa zagayen yan 16 ba, inda Kamaru ta doke Brazil, Tunisia kuwa ta ci Faransa.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like