‘Dalilan da ya sa muka ce ‘yan kasuwar arewa su daina kai kaya Kudu’



Motar dakon kaya ta fadi
Bayanan hoto,

‘Yan arewa na zargin ana tsangwamar ‘yan uwansu da ke kuduncin Najeriya

Gamayyar kungiyoyin arewacin Najeriya da aka fi sani da Northern Consensus Movement a turance, ta umarci `yayanta da ke hada-hada ko safarar kayan abinci da sauran kayan masarufi da su dakatar da kai kaya kudancin kasar.

Kungiyar ta dauki matakin ne domin nuna rashin jin dadin ta game da kisan da take zargin ana yi wa fatake `yan arewa da kuma mazauna yankin.

Shugaban gamayyar kungiyoyin, Awwal Abdullahi Aliyu, ya shaida wa BBC cewa daga farkon watan Disamba da muke ciki an kashe sama da ‘yan arewa 100, an kuma kona motoci sama da 50 a kudancin kasar.

”Wannan abin takaici ne da nuna alhini, shi ya sa muka dauki matakin, domin nuna wa ‘yan arewa cewa akwai wadanda suka damu da abin da ke faruwa, akwai wadanda za su kare mutunci da mika har da kishin halin da suke ciki.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like