Dantakarar shugaban kasar Amurka na jam’iyyar Republicans a zaben da za a yi a ranar 8 ga watan Nuwamban 2016 Donald Trump ya zargi shugaba Obama da kafa kungiyar ta’adda ta Daesh.
Kamfanin dillancin labarai na AP ya rawaito cewa, Trump ya yi jawabi ga magoya bayansa a Florida inda sau uku ya ambaci Obama a matsayin wanda ya kafa kungiyar ta’adda ta Daesh.
A baya ma Trump ya zargi abokiyar takararsa Hillary Clinton a matsayin wadda ta kafa kungiyar ta Daesh.
Donald trump ya ce, manufofin Obama a Gabas ta Tsakiya ne suka sanya kungiyar ta Daesh karfafa da ma kafata tun asali.
Babu wata sanarwa da fadar White House ta yi game da zargin na Donald Trump.