Duk Basaraken Da Ya Daki Matarsa A Bakin Rawaninsa – Sarkin Kano 



Mai Martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II ya ja hankalin masu rike da sarautun gargajiya kan dukan matansu, a inda ya ce duk mai rawanin da aka samu da laifin dukan matarsa to a bakin rawaninsa.
Muhammdu Sunusi ya kara da cewa a tsarin sarautar Kano duk mai sarauta walau dai hakimi ko dagaci ko kuma mai unguwa har ma limami da aka kai fada yana dukan matarsa to zai ajiye rawaninsa.

You may also like