‘Dukkanin gwamnoni na goyon bayan soke wa’adin daina amfani da tsofaffin kuɗi’



.

Asalin hoton, @GOVERNORINUWA

A Najeriya, yayin da ake ci gaba da taƙaddama kan wa’adin da babban bankin ƙasar ya bayar na daina amfani da tsofaffin kuɗi, gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammad Inuwa Yahaya ya ce dukkanin takwarorinsa na goyon bayan ƙarar da aka shigar na soke wa’adin.

Gwamnonin, waɗanda suka hada da na jihohin Kaduna da Zamfara da kuma Kogi sun buƙaci kotun kolin ta taka wa babban bankin burki game da wa’adin.

A tattaunawarsa da BBC, gwamnan jihar Gomben, ya ce tsarin da CBN ɗin ya kawo ba zai yi wa al’ummar arewacin ƙasar daɗi ba ganin cewa bankuna ba su wadata yanda komai zai tafi daidai ba.

Ya ce ba a faɗa wa shugaban ƙasa gaskiya ba kan abubuwan da ke faruwa na harkokin banki a arewa sannan kuma ba su buga isassun takardun kuɗi da za su wadaci al’umma ba.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like