Ebola Ta Sake Barkewa A Congo


Gwamnatin tarayya ta dauki matakan gaggawa wajen sa ido kan bakin da ke shigowa Nijeriya bayan rahoton barkewar annobar cutar Ebola a Jamhuriyyar Congo.

Rahotanni daga Jamhuriyyar Congo sun tabbatar da cewa a halin yanzu kimanin mutane 17 ne suka mutu sakamakon cutar. Idan ba a manta ba, a shekarun baya da cutar ta barke kasar Laberiya, wani dan asalin kasar ya shigo Nijeriya inda ya yada cutar wadda ta yi sanadin mutuwar wasu ‘yan Nijeriya.

You may also like