Erik: Burina Man United ta buga wasan zakarun turai a badi’



Erik ten Hag

Asalin hoton, Getty Images

Kocin Manchester United Erik ten Hag ya ce yana da burin ganin kungiyar ta samu zuwa gasar Zakarun Turai badi.

Ten Hag na fatan hutun gasar cin kofin duniya da aka yi, zai taimaka ma yan wasansa su dora daga inda suka tsaya, wurin ganin sun kare cikin hudun farko.

Ya ma ce watakila su iya lashe sarka a daya daga cikin gasannin da suke ciki.

United ta kai zagayen kwata fayinal na gasar kofin Carabao bayan doke Burnley 2-0, sannan za ta kara da Nottingham Forest a gasar Premier League a Old Trafford ranar Talata.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like