Fadan ƴan bindiga a kan “bazawara” ya yi sanadin mutuwar mutum 64 a Zamfara



Bazawara

Al’ummar garin Mutunji a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya suna cikin halin zulumi da tashin hankali, bayan asarar rayuka mafi muni da garin bai taɓa ganin irin sa ba.

Rahotanni daga garin sun ce a ƙalla mutum 64 ƴan garin ne suka rasa rayukansu bayan da wani jirgin soja ya jefa bam a wani waje da ƴan bindiga suka yi mafaka.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa saboda tsaro ya tabbatar wa BBC cewa dukkan waɗanda suka mutun maza ne, mafi yawan su ƙananan yara, sai kuma matasa da tsofaffi.

“An yi asarar rayukan da ba a taɓa samun yawan hakan ba a rana guda a garin namu kuma baya ga wadanda suka rasa rayukansu da dama sun jikkata,” ya ce.



Source link


Like it? Share with your friends!

1

You may also like