Fayemi ya sauka daga mukaminsa na minista


Kayode Fayemi, ministan ma’adanai da habaka karafa ya sauka daga mukaminsa.

Ya bayyana haka ne ranar Laraba lokacin da yake ganawa da yan jaridu a Abuja.

Fayemi shine dan takarar jam’iyar APC a zaben gwamnan jihar Ekiti da za a gudanar ranar 14 ga watan Yuni, bayan da ya samu kuri’u mafiya rinjaye a zaben fidda gwani na jam’iyar da aka sake gudanarwa.

A wancan lokacin, Fayemi ya bayyana cewa mako guda ya rage masa ya cigaba da aiki a matsayin minista bayan nan kuma zai mayar da hankali kan lashe zaben kujerar gwamnan jihar.

Fayemi ya kasance gwamnan jihar tsakanin shekarar 2010 zuwa 2014 inda ya yi rashin nasara a hannun gwamna mai ci a yanzu Ayo Fayose.

A wannan karon Fayemi zai yi takara yan takarkaru da dama ciki har da dan takarar jam’iyar PDP wanda shine mataimakin gwamnan jihar, Kolapo Olusola dake samun goyon bayan gwamna Fayose.

You may also like