Fayose Ya Yi Kira Ga Buhari Kan Ya Yi Murabus


Gwamnan Ekiti, Ayo Fayose ya sake yin kira ga Shugaba Buhari kan ya yi murabus inda ya dora alhakin tabarbarewar harkokin tsaro da na tattalin arziki a kan rashin kwarewar Shugaban.

Gwamnan ya ce, a halin yanzu farashin fetur ya kai kusan Naira 180 yayin da basussukan da ake bin Nijeriya ya haura Naira Tiriliyan 20 daga Naira Tiriliyan 12 a 2015. A bangaren tsaro kuwa, gwamnan ya jaddada cewa rashin tsaro ne ya janyo Boko Haram suka samu nasarar sake arcewa da wasu dalibai a daidai lokacin da ake fafitikar yadda za a kwato sauran ‘yan Matan Chibok.

You may also like