Gabriel Jesus ya kawo karshen kamfar cin kwallo a Arsenal



Gabriel Jesus

Asalin hoton, Getty Images

Arsenal ta ci gaba da jan ragamar teburin Premier League da tazarar maki takwas tsakaninta da Manchester City ta biyu.

Gunners ta doke Leeds United 4-1 a wasan mako na 29 a babbar gasar tamaula ta Ingila da suka kara ranar Asabar a Emirates.

Gabriel Jesus ne ya ci biyu daga ciki, karon farko da ya ci wa Arsenal kwallo tun cikin Oktoba a wasan da Gunners ta ci Tottenham 3-1 a Premier League.

Dan wasan tawagar Brazil ya ci wa Gunners kwallo biyar a wasa takwas da ya fara yi tun bayan da ya koma Emirates daga Manchester City a Yulin bara.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like