Gakpo ya yi saurin komawa Liverpool – Koeman



Cody Gakpo

Asalin hoton, Getty Images

Kociyan Netherlands, Ronald Koeman ya ce Cody Gakpo ya yi saurin komawa Liverpool ya kasa taka rawa a kungiyar da ke fuskantar kalubale a bana.

Mai shekara 23 ya taka rawar gani a gasar kofin duniya a Qatar da cin kwallo uku a wasa biyar, bayan da Netherlands ta kai quarter-finals.

Sai dai ya kasa cin kwallo a wasa shida a Liverpool, tun bayan da ya koma Anfield da taka leda daga PSV Eindhoven a watan Janairu.

”Ya koma kungiyar da ba ta yin kokari a kakar nan,” in ji Koeman.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like